Lahadi, 30 ga Agusta
Ga waɗanda an karya musu ƙarfin gwiwa, Yahweh yana kusa da su.—Zab. 34:18.
Ko da an wulaƙanta ka, kar ka damu domin Jehobah yana ƙaunarka kuma kana da muhimmanci a gare shi. Idan kana ji kamar ba ka da wani amfani, ka tuna cewa kana da hali mai kyau, shi ya sa Jehobah ya jawo ka kusa da kansa. (Yoh. 6:44) Jehobah yana ƙaunar ka sosai. Don haka, a koyaushe yana so ya taimaka maka. Yesu ya nuna mana cewa Jehobah ya damu da waɗanda ake ganin su ba kome ba ne. Saꞌad da Yesu yake duniya, ya damu da irin mutanen nan. (Mat. 9:9-12) Alal misali, da wata mata da take fama da cuta mai tsanani ta zo ta taɓa rigarsa don ta sami lafiya, Yesu ya ƙarfafa ta kuma ya yaba mata don irin bangaskiyar da ta nuna. (Mar. 5:25-34) Yesu yana koyi da Ubansa ne. (Yoh. 14:9) Wannan ya nuna cewa Jehobah yana ɗaukan ka da muhimmanci sosai, kuma yana lura da irin ƙaunar da kake masa, da bangaskiyarka da dai sauran su. w24.10 7 sakin layin na 4-5
Litinin, 31 ga Agusta
Ka auna yawan hawayena.—Zab. 56:8.
Akwai abubuwa da yawa da suka faru a rayuwar Dauda da suka sa shi kuka. Mutane da yawa sun tsane shi, kuma wasu da suke kusa da shi sun ci amanarsa. (1 Sam. 19:10, 11; 2 Sam. 15:10-14, 30) Akwai lokacin da ya ce: “Na gaji tilis saboda baƙin ciki, kowane dare gadona yakan jiƙe saboda kukana, matashin kaina yakan jiƙe sharaf da hawaye.” (Zab. 6:6) Dauda ya sha wahala sosai, amma duk da haka ya san cewa Jehobah yana ƙaunarsa. Ya ce: “Yahweh ya riga ya ji kukana.” (Zab. 6:8) Nassin yini na yau ya nuna cewa Jehobah yana ƙaunarmu sosai kuma ya damu da mu. Dauda ya ce kamar Jehobah yana auna hawayensa ne yana ajiyewa, ko yana rubuta su a wani littafi. Dauda bai yi shakkar cewa Jehobah yana ganin damuwarsa kuma yana tunawa da shi ba. Dauda ya tabbata cewa Jehobah ya san matsalar da yake ciki kuma ya san yadda abin yake damunsa. w24.12 22 sakin layi na 11-12
Talata, 1 ga Satumba
Ku gwada kanku domin ku sani ko kuna bin Yesu Almasihu cikin aminci.—2 Kor. 13:5.
Idan muka zama Kiristocin da suka manyanta, bai kamata mu tsaya a nan ba. Ya kamata mu yi iya ƙoƙarinmu don mu ci-gaba da zama Kiristocin da suka manyanta. Don haka, kada mu ɗauka cewa da yake mun manyanta, ba ma bukatar mu yi ƙoƙari. (1 Kor. 10:12) Zai dace mu ci-gaba da ‘gwada kanmu’ don mu tabbatar cewa muna samun ci-gaba a ibadarmu ga Jehobah. A wasiƙar da manzo Bulus ya rubuta wa Kolosiyawa, ya sake ambata dalilin da ya sa ya kamata mu ci-gaba da zama Kiristoci da suka manyanta. Kolosiyawan sun riga sun manyanta, duk da haka, Bulus ya gargaɗe su cewa su yi hankali don kada a ruɗe su da raꞌayoyin mutanen duniya. (Kol. 2:6-10) Wani mai suna Abafaras ya san ꞌyanꞌuwan sosai, don haka ya yi ta yin adduꞌa don ꞌyanꞌuwan su “zama cikakku” ko kuma ꞌyanꞌuwan da suka manyanta. (Kol. 4:12) Mene ne hakan ya koya mana? Bulus da Abafaras sun san cewa Kiristoci suna bukatar taimakon Jehobah kuma suna bukatar su ci-gaba da ƙarfafa dangantakarsu da shi, don abin da zai sa su ci-gaba da zama Kiristoci da suka manyanta ke nan. Suna kuma so Kolosiyawan su ci-gaba da yin hakan duk da matsalolin da suke fuskanta. w24.04 6-7 sakin layi na 16-17